Labaran Safiyar Jumma'a 25/01/2019CE - 18/05/1440AH. Cikakkun labaran Alhaji Atiku Abubakar ya ce zai dawo da martabar Najeriya da ta zube. Boko Haram sun kashe mutum 2 a Yobe bayan da sojoji suka tsere. Kabilar Ibo mazauna jihar Kano sun nuna goyon bayansu ga Ganduje. Dandazon mutane sun hallarci wurin kaddamar da yakin neman zaben Shugaba Buhari a jihar Enugu. Wasu yan fashi da makami sun kai farmaki a wani bankin Polaris da ke Oke Ejigbo, Ila Orangun da ke jihar Osun. Kotun daukaka kara ta maida wa Donald Duke takarar sa ta kujerar shugaban kasa a jam'iyyar SDP. Shugaba Buhari ya bayyana cewa, zai samar da tashar Jirgin kasa a jihar Kebbi. Wasu kungiyoyi na son kasashen Turai su sanya wa Obasanjo Takunkumin shiga kasashen waje. A jamhoriyar Nijar wani rikici ne ke neman barkewa a hukumar hajji da umara na kasar. Kasar Amurka ta ce ba ta goyon bayan kowani dan takara a Najeriya. Mahaifiyar fitaccen dan kwallon kafa na Najeriya,...
Muryar arewa 24 Munbude wannan Gidan Domin wayer dakan Al ummar arewa dama Nigeria gabaki daya.